Furar Danko Book 02 Page 42

 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲





  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗





           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻



      𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣2️⃣



______________



*3 DAYS CLASS*


Ko kunsan cewa duk shekara ana samun rarar kudade a turai wanda ake cewa *unclaimed scholarship funds?* Kunsan irin ayyuka Jobs da zaku nema ku samu daga Nigeria zuwa kowace kasa? Ana samun rarar kudinne sakamakon  rashin neman scholarship da bama yi, mun bude 3 days class don koya muku yadda zaku samu scholarship a kasashen waje, da yadda zaku nemi karatu da yadda zaku nemi Aiki Skills or unskills Job daga gida Nigeria zuwa kowace kasa da takardun secondary diploma ko degree da yadda zaka canza kasa Relocating daga Nigeria zuwa kowace kasa, Canada, Us, etc a tuntubeni 


Class ze fara ranar jumaa insha Allah 


WhatsApp group 👇👇👇


https://chat.whatsapp.com/E8Lzqogsm1nAFy1feTwbmA


WhatsApp 08144147273


👉 Masu bukatar tafiya da kudinsu ba scholarship ba, Muna yin study & work ko working visa, a takaitaccen lokaci, working visa Qatar munayi a sati daya, Canada study & working visa a 4 to 5 months, Oman working visa a 7 days insha Allah, Maxico Tour visa 1 month


_______________



........Kuka take sosai a gaban mijin nata da ayanzu al'amuransa ke bata tsoro matuƙa. Gaba ɗaya ya sauya mata, sauyawa irin wadda bata taɓa zato ko tsammani ba. Kai koda a mafarki ko lissafin rayuwa bata taɓa tunanin itada Sufiyanun nata zasu kasance a irin wannan ajin ba. Amma a yau sai gashi wai harda mata kishiya sa'ar jikokinta da wannan shekarun nata tsofai-tsofai. Kuma ko kunyarta baya ji yake soyayyarsa kamar wani ƙaramin yaro.

        Baba Garko da tunda ta shigo ta zauna bai ko ɗaga kai ya dubeta ba sai ma wayoyinsa da yake hankali kwance. Daya gama wannan zakaga wata ta shigo. Cikin jin gundura da kukan da take rera masa ya ce, “Amma dai kin san kina damuna ko? Please bana son damuwa idan kukanki zakiyi zaki iya bani waje”.

    Sake ɓarkewa tai da sabon kuka kamar wata ƙaramar yarinya. A dai-dai nan akai knocking ƙofar falon, ɗan jimmm yay yana kallon ƙofar kafin ya ce, “Ko waye ya shigo”. Mai aikin amaryarsa ce ta shigo a rikice, amma hakan bai hanata kaiwa tsugunne da ga bakin ƙofa ba ta gaisheshi cikin girmamawa sannan ta ɗora da faɗin, “Alhaji aunty amarya ce bata da lafiya, tun ɗazun kuma ta hana azo a sanar mak...” ai mai aikin ma bata ƙarasa rufe baki ba ya miƙe zaram ko nauyin tsufarsa baya ji. Ƙofar ya nufa a hanzarce, Dada da kanta ya nema tarwatsewa ta bisa da kallo galala, wani irin tuƙuƙin baƙin ciki na sake turniƙe mata zuciya. Ba'a ko rufa minti huɗu ba sai gashi ya shigo a rikice, ko kallon inda take baiyi ba ya shige bedroom ɗinsa. Cikin ƴan sakanni ya sake fitowa ya fice hannunsa riƙe da key ɗin mota ya canja zuwa jallabiya. Kasa motsawa tayi a wajen har sai da taji ƴar hayaniya na tashi ta miƙe jikinta na rawar ɓacin rai ta leƙa ta window. Akan Baba garko da ke rungume da amaryarsa ita kuma tana faman yarfe hannu tana kuka idanunta suka fara sauka. A take zuciyarta ta ayyana mata haihuwa. Sake dugunzuma zuciyarta tayi har tana jin jiri na neman kwasarta, batama san sanda ta sulale a wajen ba ta zube saman kujera jaɓar wasu zafafan hawaye na wanke mata fuska, sai kuma ta ɓarke da kuka. Tunda take a rayuwarta, bata taɓa shiga matsanancin baƙin ciki da tashin hankali irin na wannan gaɓar ba. A tsahon rayuwar ƙuruciyarta ko firar kishiya bata so, kai ko ƙawa ko cikin ƴan uwa akaima wata kishiya daina zuwa gidan mutum take saboda yanda ta tsani kishiya. Amma a yau sai gata da ita a wannan shekarun nata, harma da ciki na haihuwa.....


       (🤣🤣🤣🤣🤣 Kar kuce dariyar mugunta nakema Dadaras😜)


         ____________★


     Tun Ummah na ɗaukar al'amarin ta ƙarami harta fahimci ya wuce da saninta. Kuka ma da hawaye yanzu ta kasa yinsa. Ƴan gidansu sunzo sai dai me suma ƙarewa sukai da fita da gudu harda masu faɗuwa. Wajen Abba suka koma kowa na maida numfashi, yayanta cikin damuwa ya ce, “Anya ba aljanune suka shigi Yahanasu ba Yaya Mika'il”.

    Cikin ɗan taɓe baki Abba yace, “Idan ma sune wajen biɗar baƙar tambayarta ta kwaso su. Ballema bana jin hakanne. Nafi ƙyautata zaton ƙaiƙayine ya koma kan masheƙiya. Ni yanzu jibirin ban san yanda zanyi da wannan matar ba. Gaba ɗaya ta firgitamin iyali sun kasa sakewa kowa sai zaman ɗaki”.

      Cikin damuwa Jibirin yace, “Amma yaya bai kamata kace haka ba. Ƙilama cikin matanka wata taimata haka kasan dai mata akan kishi”.

    “Wane matan nawa? A'a ƙarya haramun. Ai duk cikin iyalina babu fanɗararre irin Yaha. Nasan halin kowacce a cikinsu da abinda zata iya. Na jima ina zarginta dama da shigen-shigen nan kawai dai ban taɓa gani da idona bane shiyyasa ban kafa hujja ba. Amma a yanzu na gama fahimtar komai. Ko wannan halin da kaga tana cikin sihirin da taima Aliyu da matarsa ne ya dawo mata...”

           “Aliyu kuma Yaya? Aliyu Aliyu dai namu na nan?”.

       “Shi ɗin fa”.

   “Ikon ALLAH! To shi Aliyu dake matsayin ɗanta kuma zatama asiri. Miye ribarta kenan?”.

             “Oho mata, ita ta sani”.

        Sosai al'amarin ya girmi kan kowa. Cikin ƙarfin hali Zaidu ya bada shawaran to ko za'a samo malamai suyi addu'a ne. Dan wannan yanayin nata abin tashin hankali ne ga kowa tunda gashi hankalin kowa a tashe, shi wlhy yanzu haka baya jin yau ɗin nan zai iya barci lafiya saboda ganin wannan mummunar halitta da Ummah ta koma. Abba dai yace shi babu ko sisinsa a nema mata lafiya. Hasalima ya kirasu ne su wuce da ita dan bazai iya ba. Hankalinsu ya tashi matuƙa, dan sukam bazasu jajibi wannan halittar ba sukai cikin iyalinsu suna zaune ƙalau. Dan haka suka dage bashi haƙuri da roƙo da magiyar ya barta a ɗakinta cikin ƴaƴanta harta samu lafiya sai aji dalilinta na wannan mummunan al'amari, idan ma matakin sai ɗauka sai ya ɗauka. Anfi ƙarfin Abba ne kawai, dan haka yay shiru. Su suka fita suka zo da malamai, da ga tsakar gida suka tsaya aka kwala mata kira ta fito. Su kansu malaman sai da suka zabura da ganin mummunar halittar dake tunkarasu, ganin tana yo kansu gadan-gadan sukaji fa dauriya ba tasu bace. Ai tuni suka dafe kawuna kowa ya ara cikin ta kare yana jan kula'uzai. Bayan su an sake kawo wasu malaman amma fa kowa yazo yana tozali da Umma sai dai a tsincesa waje ya dafe ƙeya. Al'amari kamar wasa sai ƙara faɗi yake. Dan takai ƴan jarida daga gidajen rediyo har sun fara zuwa neman labari. Sai dai suma fa suna shigowa sukai ido huɗu da Umma labarin bai ɗaukuwa garesu sai ƴar reren gudu...

      Tsabar tashin hankali da hawan jini Umma ta koma ko gani batayi da ƙyau. Barci kuwa ya ƙauracema idanunta gaba ɗaya. Cikin ƙanƙanin lokaci tai wata irin muguwar rama mai ban tsoro. Babu abinda ke ɗaga mata hankali sai ganin ƴaƴanta suma gudunta suke da mijinta da ta ɓata tsahon shekarun rayuwarta tana faɗa da faɗi tashi a kansa. tana son jin halin da Hajiya Naqiba take amma babu hali. Rayuwa ta mata duhu, duhu irin wanda ko tafin hannunka baka iya gani, duhu irin wanda zuciya kanta bata iya tuna komai sai ƙunci da ciwo mai raɗaɗi. Hatta salla yinta kawai take amma bata ma sanin mitake yi a cikinta. wanka kam bama'a maganarsa dan tashin hankali. abinci dama yanzu ƙofar ɗaki Abba ke zuwa ya ajiye mata saboda kowa tsoro yake ji, shi kansa dai tausayin rai ne ke sakashi yin ƙarfin halin ajiyewar kawai dan an hanata fitowa.....


        *_★UK★_*


    Sosai tasha barci, dan ko da lokacin salla yayi da ƙyar ya iya tashinta tayi ta sake komawa. Bata tashi ba sai gab da la'asar. Yana falo suna kicimilli da ɗansa ta fito. Tsaye kawai tai tana kallonsu har bata san tana murmushi ba. Mayataccen ƙamshinta ya fargar da Smart kasancewarta a wajen. Zaune ya tashi da ga kwancen da yake yana ɗaga AA dake sukuwa a saman cikinsa. Cikin lumshe ido da sakar mata murmushi ya ce, “Kin tashi?”. Cikin falon ta ƙarasa takowa tana marairaice fuska. Hannunsa ya miƙa mata alamar tazo garesa. Babu musu ta ƙaraso, ya riƙo hannunta ya zaunar gefensa yana mai rungumota ta gefen jikinsa kanta a saman kafaɗarsa. AA dake neman haye mata jiki ta dungurema kai batare da tayi magana ba. Smart dake kallonsu da murmushi ya shafo fuskarta da faɗin, “Yaya jikin naki?”.

       “Ba sauƙi”.

    Ta bashi amsa cikin tura baki.

Sosai ya waro idanunsa waje. “Ba sauƙi fa Nooru Nisa”.

      Fuska a gimtse ta ce, “Eh mana dan ni dai jikina ciwo yake mun har yanzu”.

     “Kai Madam bansan ragwantaka fa. Ni da nake shirin yanzu a sake tafiya yaƙin ƙasa da ƙasar again.”

           “Dawa?!”.

      Yanda tace dawa ɗin cikin waro idanu da ƙwaɓe fuska kamar zatayi kuka ya sashi kwashewa da dariya. Mintsini mai zafi ta sakar masa tana miƙewa. Ya riƙe wajen da sauri yana yamutse fuska da faɗin, “Wai ALLAH na! wannan zalincin fa? Kefa kin iya mugunta”.

    Gwalo ta masa tana dariya, ta ce, “Mugayen ai da yawa kai ne malamina”. Tai wucewarta kitchen Dan yunwa takeji. 

        “Haka kika ce ko? Ba komai zan rama ne”.

    Dariya ta shige tanayi, babu jimawa ta fito ɗauke da apples data yayyanka a ƙaramin bowl. Ƙasa ta zauna dan taji daɗin miƙe ƙafa. Smart dake binta da kallo ya ce, “Badai wannan ne abincin ba?”.

        Muryarta a marairaice da shagwaɓa ta ce, “ALLAH bakina babu daɗi, ina son naci kozai washe. Sannan wannan ɗin ma ni kam ya isheni”.

     Idanu kawai ya tsira mata yana kallonta. Ta ɗan hararesa da faɗin, “Kallon fa?”. Murmushi yayi da janye idanun nasa cikin yin luuu da su. Sai kuma ya sake zuba mata su cikin yanayin kasala. “Yarinyar nan anya kuwa?”.

             “Anya kuwa mi?”.

        “A'a ni bance komai ba. Kawai dai dama sai nake ga kamar fa wannan karon ma kin amshe ne, kin san fa ni bana saɓa saiti a zahirin fili wasa da na ɓoye”.

     Da farko bata fahimci mi yake nufi ba. Sai da tai ɗan shiru sai kuma ta dago ta hararesa. Dariya ya ƙyalƙyale da shi, zai sake magana ta tura masa Apple ɗin data tsiro a bakin tana sake harararsa. “Kai dai ALLAH ya shiryeka wlhy”.

         Murmushinsa ya cigaba da yi shi dai, koda ya shanye apple ɗin data saka masan sai ya sake matsowa da buɗe baki wai ta ƙara masa. Kafaɗa ta maƙe alamar anƙi ɗin. Ya bata fuska cikin yanayin shagwaɓa. “Kina sha, kina bama AA ni kuma sai a wareni. ALLAH sarki nima da Ammah na kusa da banga haka ba. Bari na kirata na faɗa mata”. 

      Da sauri ta fisge wayar ta tura ƙasan ƙafafunta. Sannan ta tsiro apple ɗin ta tura masa abaki tana harararsa. “Mai kwaɗayi, kai yanzu in an barka saika faɗa?”.

         “Sosai kuwa. Harma da Daddy da Abba duk zan kira, ince tunda kika zo baƙya kula da ni.”

     “Sharri Master kenan. Daka kasheni dan ina jin kunyar Abba sosai ALLAH.”

     “Ni kuma baƙya jin kunyata ko?”.

Murmushi tayi tana sakama AA da ke tsaye jikinta yana wasa da gashinta apple ɗin a baki. Cikin basar da zancensa ta ce, “Da kai Daddy ya haɗa baki kuka kawoni nan ko?”.

            Kwance ya kai yana ɗora kansa a saman cinyarta, sai da yay ƴar dariya da tsokano AA ya ce, “Nikam babu ruwana. Daddy ne yay miki wayonsu na manya saboda yana jin tausayina. Shekaranjiya dai muna magana da shi yake cemin akwai saƙo da zai aiko min da shi, idan kuma ya samu shigowa London to, dan zaije Manchester city ne”.

     “Lallai ma Daddy nice saƙon yake nufi ko mi! Sai kace wata kayan wanki”.

   Dariya sosai Smart ke ƙyalƙyalawa har AA na faɗawa jikinsa shima yana tayashi. Sai kawai Lulu ta zuba musu ido tana kallo. Sai da sukai mai isarsu ya jiyo yana kallonta. Ganin yanda ta zuba musu ido ya ɗan ɗage gira da faɗin, “Kallon fa Madam”.

            “To ba dole na kalleku ba naga kun zare. Wai nikam dama kana dariya har haka? Amma da kaita tsuke fuska kamar wanda akaima saƙon mutuwa!”.

     Kansa kawai ya shafa yana murmushi baice mata komai ba. Itama sai ta share ta cigaba da shan Apple ɗin ta. Lokacin-lokaci tana saka masa a baki shi da AA da ke saman jikinsa yana wasa da ƙasumbarsa.......✍️


        _🚴Ya kamata mu taya Ummah da Addu'a 🥱🥱🥱_




_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*


FURAR DANKO

Billyn Abdul


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at👇


1487616276 

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070



*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥




*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments