Ingarman Namiji 17-18

 Page 17 & 18


____zekunnah kenan wayarshi tafara rurin neman d'auki d'auka yayi tareda Kara wayar akunne

batareda yace komaiba..acan bangaren sulaiman kuma jin and'aga wayar yasashi fara magana domin

yasan bazeyi maganarba tin yayi shiru.."big man kanajina kuntaso kuwa?"No miyafaru ne? Yatambaya

cikin daddan vocie dinshi.."wlh yanzu GR yakirani yakecewa yakiraka baka d'agaba Kuma yawar Ahmad

baya tafiya Wai muyi sauri muzo yau zamushiga aikin domin matsalar takaru daga yadda mukasanta Dan

Allah kuyi sauri muwuce domin kukad'ai nakejira please.."ok badamuwa gamunan zuwa yafad'a tareda

katse wayar yamayarda computer shi wurinta kana yak'arasa shiryawa yafita.

Sulaiman abukinsune tin a school shida ma,aruf da yaseer Amma su bagarinsu d'ayaba suma zasu

bayyana idan lokaci yayi bayansuma akwai wasu mutanen dasu,nansu ze,iya bayyana agaba inafatar

kungane

Aperlo yasamu su Ahmad najiranshi suka rankaya suka fita zuwa pert d'in iyayensu daga big mom har

anty amarya addu,a sukayi masu sosai kana suka tifa zuwa pert d'in kakarsu alhajiya Nene ikon Allah

kenan.

Koda sukaje Nene nahakimce aperlo me,aikin big mom namata tausa..d'agowa tayi tana K'are musu

kallo domin tafe suke apelon cikin takon isa da tak'ama tafiya sukeyi irinta gwarazan maza cikin kuzari da

haiba daganinsu kaga cikakken mazaje masu jini ajika.

Zama sukayi dukkansu akusanta yayinda sadeeq yad'ora kanshi acinyarta suma suka zuba Mata Ido

bawanda yace komai..baki Nene tatab'e kana taguntsura goronta takaibaki kana tace "ohhhhh nidije na

naga abunda keshan jininjikina yanzu ku Dan Allah Dan annabi Dan kuga su wad'ancan sha,shashun

iyayen naku sun zubamuku ido shine kukamik'e Kuma azaune sekace bamazan kirkiba. tak'arasa zancen

tana kallan sadeeq daya d'ago shima Yana kallanta cikin alamar tambaya.. Ahmad ne yayi k'arfin halin

cewa"kamarya bamazan kirkiba Nene ?

"Ahhhabb yoto Ina mazan kirki anan kowanneku ze iya nome gona 10 alokaci d'aya Kuma yayi Mata

kyakkyawan banruwa tayadda za,asamu yabanya me kyau..Amma kunkasa kozancen auren ma bakwayi

dakuda iyayen naku bansan miye nufikuba koso kukeyi Sena mutu ohooo.

Shuru sukayi Mata bawanda yace komai domin duk basugano inda zancenta yanufaba se yanzu.."kunyi

shiru kunk'yaleni sekace Ina magana da kurame.."No Nene bafahaka bane zamuyi idan lokaci yayi Amma

kina mana zencen aure tinyanzu dukama nawa muke cewar Ahmad yak'arasa zancen yanadan yamutsa

fuska..

"Nono Kuma nonon uwarka kajimun d'anbanzan yaro daga maganar aure sekakawomin zancen wani

nono kanasan nonon ne kak'i kayi aure kasha harka yau naji bakantaccen yaro tafad'a tareda

dumgurewa Ahmad goshi.

Ido yazeed yazaro Jin yadda Nene tasauyawa Ahmad zance lokaci d'aya tareda saken murmushi gefen

baki Wanda yak'arawa kyakkyawar fuskarsa kyau da kwar jini..shidai Ahmad baki kawai yasaki Yana

kallan ikon Allah yakasa cewa komai yayinda sadeeq ketintsirewa da dariyar shak'iyyanci..kallanta

tamayar ga yazeed kana tace"yau aidole kamun dariya Amma ai tind'azu nake magana bakace komaiba

kaini wlh ma inatantamar lpyr ku dukanku domin indai lpy qalau kuke to doline kubuk'aci mace dominni

wlh Allah kab azuri,ata ba raggon maza Kuma ban haufi lusarin damace zata bawa tsoroba seku Amma

nasan mizanyi akai doline nad'au k'wk'kwaran mataki akanku wlh dagaku har iyayen naku.. tafad'a tana

hura hanci tareda ture dankwalin kanta gaba duka kwakkawar sumar kanta tabayya Takoma fara sool.

Murmushi kawai sukayi atare kana sukamik'e tareda gaya Mata zasu koma wurin aiki..Aiko tak'ara

hayyak'o musu damasifa tana fad'ar nankawai sukafi kauri sudai basuce komaiba abinka da miskilai seda

tagaji Dan kanta kana tamusu addu,a dafatan alkhairi kana sukafice..sunafita sukatarar yaransu duk

sunkaraso sunajiransu motoci suka shiga tareda barin gidan Basu zarce ko,inaba se gidansu sulaiman

tinkamun suk'arasa sukamai waya shiyasa yafito suna k'arasawa yashiga sukawuce se filin jirgi...karfe

9:30am Dede jirginsu yatashi se birnin tarayya Abuja..

Yayinda k'arfe Tara Dede akasallami sumayya daga asibiti sukayo gida bayan ansha famada,ita akan

bazataje gidaba gidan anty lele zata koma anyi,anyi Tak'i yadda seda taji hajiya mama nawayada big

mom tana gayamata su Ahmad suntafi kana tayadda zata koma gida murmushi kawai Abba yayi dominsu

duk atunaninsu muta,nentane basusan ta,asar datayiba.

Unguwar Gama B Kano

SAURAT ce zaune itada Mami mahaifiyata kenan.."Wai SAURAT miyasa kikesaka Wannan kayan bana

hanakiba eye? "Baki taturo gaba tareda duban kayan jikinta rigace iyakarta gyiwwarta Kuma batada

wadataccen hannu kana saga2 take har underway d'inta anaganin kwancinsu."nifa Allah zafi nakeji

Mami banasan Wannan manyan kayan Allah.."tofa ฀ keyanzu kokunya bakyaji dalibanki suzo susameki

ahaka idan sunganki cikin zumbulelen hijab se arantse da Allah wata kamilace ke..baki taturo tareda

b'ata fuska cikin shagwaba take fadar "haba Mami yanzuni ba kamila baceba? "Ehhh lallai SAURAT

kekamilace Amma Bata fanni suturta jikiba Zakitashi kinemi suturar kurki kisaka kosena makeki..tashi

tayi tana k'uk'unai tareda bubuga kafafuwanta ak'asa duk ilahirin jikinta yad'auki girgiza..Ido nazaro

kamun nasake murzasu Ina Kare Mata kallo lallai SAURAT takai duk inda cikakkiyar mace kekai domin

tsakanin SAURAT SUMAYYA dakuma BUDURWAR jeji narasa wacce tafi wata diri kyau dakuma.....nayi

shiru฀฀ahakan tawuce bedroom d'inta tareda rufe k'ofar Kai kawai Mami tagirgiza tareda rokon Allah

yakare Mata tillon Yar tata.

Abuja

Tsaitsaye suke cikin wani katon office gadukkan alamu nanne office d'in GR kowanne ak'ame Yana

saura,rar abunda megidan Nadu kefad'a

"kusani Wannan shine damar damuka samu akansu domin duk sakonda suke turo Mana alokaci d'aya da

mabanbanta nomber da wurare daban2 Dan su hargitsa Muna lissafine karmu gano shirinsu sund'auka

muma marasa tinanine kamarsu shiyasa mukayi k'wak'waran bincike akan komai nasu Kuma insha Allah

yanzu munyi Shirin tukararsu akowanne yayi bagudu bajadaba kusani domin sugano yanlek'en asirinmu

yanzu hakan farautarsu sukeyi Kuma Kunga bakayan aiki ataredasu inafatar kungane bayanina.?

"yers Sr suka fad'a gabad'aya.."Masha Allah tinda kunfahinta yanzu Kai sadeeq da sulaiman zaku

jagoranci shiga jejin yobe state yazeed da Ahmad sujagoranci jejin barno state Yusuf da manir zaku

yagoranci jejin Zanfara state yanzu kowa yad'ibi yaransa ku d'au hanya Allah yakareku.."ameen y Allah

suka ansa atare..kana suka fice kowanne da,abunda yakesak'awa aransa suna masujin zafin rabasun

da,akayi wurin tafiyar..ahakan kowa yad'ibi yaransa suna masuyiwa juna fatan nasara sukarabu inda

sadeeq da sulaiman su d'au hanyar yobe yayinda yazeed da Ahmad suka d'au hanyar barno...

Asauka lpy matafiya.

Gaskiya inbaga comment me ratsa zuciya ba bazak'uga update ba har week d'innan yak'are

Free page yakusa k'arewa idan kinshirya karatun INGARMAN NAMUJI to kihanzarta sayan naki tahanyar

datadace #500 kachal ฀ idan kintashi siya Zaki iya yimun magana tawannan nomber 07037092176

Autar alheri✍฀

ALHERI WRITERS ASSO

 A.W.A

https://www.facebook.com/100186388252056/posts/

_______________

฀ INGARMAN NAMIJI

No comments